Mawaƙin ya wallafa hakan ne a shafinsa na Instagram cewa yanaa so ya yi zazzafar waƙa don yowa Atiku kiranye.

Fitaccen mawaƙi kuma jarumi a masana antar fina finan Hausa Adam Zango ne ya bayyana hakan cikin wani faifan bidiyo da yayi.

Ya ce tunda aka yi zaɓe tsohon ɗan takarar shugaban ƙasa Atiku Abubakar ya tafi dubai, kuma yana son yin waƙar ne don yi masa kiranye.

Ya cigaba da cewa a wannan lokaci ba su samu abinda suke buƙata ba a dangane da zaɓen da aka yi a shekarar 2019, don haka ya nemi masoyan Atiku ƴan Najeriya da kowanne mutum guda ya tura naira 500 don yiwa Atiku waƙa.

Hakan na zuwa ne kwana ɗaya rak da tattaunawarmu da mawaƙi Dauda Kahutu wanda aka fi sani da Rarara da ya nemi masoya Buhari su tura naira 1000 kowanne don yiwa shugaban kasar waƙa tare da nuna ayyukan da ya yiwa kasa.

One thought on “Adam Zango zai yiwa Atiku waƙar kiranye idan kowa ya tura 500”

Leave a Reply

%d bloggers like this: