Wakilan kasashen duniya sun yi wani taro na duba hanyoyin kawo karshen rikicin da ke faruwa a Kasar Ukraine.

Masu bayar da shawara kan harkokin tsaro na ƙasashen da kungiyoyin duniya sun kammala taron tattaunawa a Jeddah dangane da abubuwan da ke faruwa a kasar Ukraine.

A ranar Asabar 5th ga watan Agusta wanda aka yi na kasashen duniya 40 da kuma wasu kungiyoyin duniya ne su ka halarta.

Wakilai a zauren Majalisar Dinkin Duniya sunhalarci taron.

Zaman ya gudana ne karkashin jagorancin karamin minista sannan mai bayar da shawara kan harkokin tsaro Dakta Mosaad Bin Mohammad Al-Aiban.

ki

Wadanda su ka halarci taron sun yabawa kasar Saudiyya bisa gayyato mutane sannan ta shirya tare da tsara taron a cikin kasar.

Taron na zuwa ne a wani bangare na sake daura damara tare da cigaba da kuma ƙara kaimi wanda yarima Mohammad Bin Salman Bin Abdulaziz ya aiwatar, kuma masarautar saudiyya ta shiga tsakani tun a watan Maris na shekarar 2022.

Kasashe da kungiyoyin da su ka aike da wakilcin sun hada da, Argentine Australia, Bahrain, Brazil, Bulgaria, Canada Chile, da kuma ƙasar China.

Sauran su ne hadaddiyar daular Comoros, Czech, Denmark, Egypt, Estonia, European Commission, European Council, Finland, Germany, French Republic, India, Indonesia, Japan, Hashemite, Jordan Latvia da kuma Qatar, Korea, South Africa, Lithuania.

Haka kuma akwai Italian, Kuwait, Netherlands, Norway, Poland, Korea, Romania, Turkey, Hadaddiyar daular larabawa, Amuruka, majalisar dinkin duniya da kuma kasar Ukraine.

Mahalarta taron sun gamsu da cigaba da tattaunawa tare da bayyana ra’ayi, domin samar da hanyoyin na dorewar zaman lafiya.

Sannan sun gamsu da yadda aka samar da cigaba a zaman da ya gabata.

Leave a Reply

%d bloggers like this: