Connect with us

Rahoto

Ko a wane Hali likitoci suke ciki A jihar Kano ?

Published

on

Rahoton Jamilu mohd yakasai

Ma’aikatan lafiya nacikin furgici a jahar kano

Watakila a samu koma-baya a yakin da ake yi da annobar korana, sakamakon ja da baya da likitoci suka yi a asibitin koyarwa na Mallam Aminu da ke Kano.

Likitocin dai su na kukan rashin kayan kariya, lamarin da suka ce yana jefa su cikin hadarin harbuwa da cutar korona.

Likitocin, wadanda ke rukunin masu neman kwarewa a asibitin koyarwa na Mallam Aminu Kano sun samu kan su a wani mawuyacin hali a Kano, musamman yadda dawainiya ta karu ta kula da marasa lafiyar da ke kwarara asibitin.

Sannan lama’rin ya ta`azzara a dan tsakanin nan, da aka samu karuwar mutuwar mutane masu yawan shekaru.

Dokta Abubakar Nagoma, shi ne babban jami’in kungiyar likitoci masu neman kwarewar, reshen asibitin Mallam Aminu Kano, wanda ya ce aikin da suke yi ya karu, ga shi suna fama da karancin kayan kariya.

”Mun shiga furgici, marasa lafiya na karuwa kullum tururuwa suke yi gashi an samu mara lafiya da ya yada wannan cutar a asibitin”

Aiki ya tsaya cak saboda baka san me zaka taba ko ka gani, cewar Dokta Abubakar.

Shugaban kungiyar likitocin ya ce hukumomin asibitin sun yi bakin kokarinsu wajen samar da makarin fuska da safar hannu da kuma man kashe kwayar cuta na sanitaiza, amma kayan kare jiki baki daya bai samu ba.

Don haka ala tilas, likitocin sun ja da baya, ba kuma yajin aiki suke yi ba, suna kokari ne su kare tasu lafiyar da ta iyalansu da kuma abokan aiki.

Su ma hukumomin asibitin Mallam Aminu Kanon sun tabbatar da batun kalubalen da ake fuskanta a asibitin.

Farfesa Musa Babashani shi ne shugaban sashen ba da magani da ke shaidawa BBC matsanancin hali da suke ciki.

”A kasa da duniyar ma baki daya ana fama da rashin kayan aiki, amma hukumar asibiti da daidaikun mutane na kawo agaji”

Ya ce ana samun tallafi amma gaskiya ba sa isa, amma sun tattauna da kwamitin da gwamnatin Tarayya ta aiko domin lalubo hanyoyin kawo musu dauki.

Asibitin mallam Aminu Kano dai ya zama rumfa sha shirgi, musamman ma yadda marasa lafiya ke zuwa neman magani daga sassa daban-daban na Najeriya da wasu kasashe makwabta.

A wannan lokacin da aka rufe asibitoci masu zaman kansu saboda cutar korona durkushewar asibitin ka iya zama babban koma-baya.

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari da gwamnatin jihar Kano, duka sun yi alwashin tallafa yin tsayin-daka wajen ceto rayukan al`ummar jihar Kano daga annobar korona.

Wadannan ra’ayoyi da aka wallafa a wannan rubutun na wanda ya rubuta ne.

Click to comment

Leave a Reply

Rahoto

Akwai Yiwuwar Kasuwanci Ya Tsaya Cak A Najeriya

Published

on

Yayin da ya rage saura kwanaki goma kacal a dakatar da karɓar kuɗaɗe da aka sauyawa fasali a Najeriya, kasuwanci na fuskantar barazana cikin waɗannan kwaanaki.

Gwamnatin tarayya ta sauya fasalin naira 200, 500 da kuma naira 1,000 tare da sanya wa’adin ƙarshen watan Janairun da mu ke ciki a matsayin ranar karshe da za a daina karɓar tsofaffin kuɗi.

A sakamakon hakan ya sanya wasu da dama daga cikin ƴan kasuwa musamman a Kano cibiyar Kasuwanci, su ka tsayar da ranar Laraba a matsayin ranar da za su rufe amsar tsofaffin kuɗin da aka sauya.

A ɓangaren ƙananan ƴan kasuwa kuwa sun sanya ranar Talata domin daina karɓar kuɗaɗen tare da ƙoƙarin shigar da waɗanda ke hannunsu zuwa gaba.

Wajen da gizo ke saƙar shi ne, har a yanzu babu wadatattun sabbin nairar a hannun mutane.

A wani bincike da Matashiya TV ta yi, ta gano wasu yankuna da ake sanya wani kaso kafin shigar da kuɗi ga masu sana ar POS.

Wata majiya taa tabbatar da cewar,ana karɓar naira 3,000 a matsayin caji idan mutum ya na so a tura masa naira 100,000.

Ko za a iya samun wadataccen kuɗin zuwa watan Fabrairu?

Tambayar da wasu mutaane ƴan Najeriya ke yi bayan ƙorafin rashin wadatar sabbin kuɗi a hannunsu.

Sai dai bankin Najeriya CBN ya ce ya kafa wani tsari da zai dinga karɓar tsofaffin kuɗin a mataki na ƙananan hukumomi na Najeriya.

Ko sabon tsarin na CBN ya fara aiki?

Har yanzu mutane na kokawa a dangane da batun sauyin kuɗin yayin da bankune ke cike don shigar da waɗand ake hannunsu zuwa asusun ajiya.

Ta yaya kasuwanci zai tsayaa cak a Najeriya?

Duba ga rashin wadatar sabbin kuɗin a hannun jama’a tare da ƙoƙarin mayar da tsofaffin zuwa bankuna, hada-hadar kasuwar na iya samun naƙasu duba ga yanayin da aka saba yin kasuwanci.

Da yawan ƴan kasuwa na amfani da takardar kuɗi wajen saye ko sayarwa a kasuwannin Najeriya.

Haka kuma mutane da ke siyayya na har yanzu akwai ƙaraancin kuɗaɗe a hannunsu yayin da ya rage saura kwanaki goma a dakatar da karɓar kuɗin a hukumance.

Ko za a iya samun sasdauci?

Akwai yuwuwar hakan duba ga cewa gwamnati ba ta yi aalbashi ba kuma ana kyautaa zaton biyan albashin da za a yi za a yi amfani da saabbin kuɗi qajen biya.

 

Continue Reading

Rahoto

Dala Bilayan 12 ake asara a Najeriya Sakamakon Rikicin Makiyaya da Manoma

Published

on

An samu rahoton asarar akalla dala biliyan 12 a Nijeriya, sakamakon rikicin manoma da makiyaya da ya mamaye sassa daban daban na kasar.

Daraktan kungiyar sa kai ta Mercy Corps, Ndubisi Anyanwu,ne ya sanar da hakan a ranar Talata a zantawarsa da manema labarai jim kadan bayan ganawa da jami’an gwamnati a garin Makurdi.

“a cewarsa sun yi kiyasin asarar akalla $12b a kowacce shekara sakamakon rikicin makiyaya da manoma. “Wannan wani babban al’amari ne kuma da zai iya shafar kasar baki daya,”

Anyanwu ya kara da cewa akwai bukatar a mayar da hankali kan rikici tsakanin makiyaya da manoma, yana mai cewa wannan ne ma dalilin da yasa kungiyar ta shiga cikin lamarin.

Ya yi nuni da cewa kungiyar Mercy Corps, da aka samar da ita karkashin hukumar USAID, ta mayar da hankali kan gina zaman lafiya na watanni 60 a Benue da wasu jihohin jihar.

Tun farko, shugabannin kananan hukumomi a jawabansu daban daban sun lissafa rashin aikin yi, rashin ababen more rayuwa daga cikin dalilan haddasa rikicin makiyaya da manoma.

Continue Reading

Rahoto

An samu asarar rayuka 415 a Najeriya daga watan Yuli zuwa yanzu

Published

on

Wasu Alkaluman bincike na nuni da cewar akalla mutane 415 aka kashe a Najeriya a watan Yulin da ya gabata sakamakon hare hare da kuma tashin hankalin da ake cigaba da samu a cikin kasar.

Rfi hausa ta rawaito cewa Wata kungiya da ta kira kan ta ‘Nigeria Mourn’ tace an fi samun kashe kashen dake da nasaba da hare haren Yan bindiga da rikicin yan tada kayar baya da kuma barayin shanu ne a Jihohin Kaduna da Borno da Katsina.

Alkaluman kungiyar sun ce daga cikin Jihohi 21 da aka kashe mutane 415, Jihar Kaduna ke sahun gaba da mutane 139, sai Barno mai 113, Katsina na da 80, Kogi 17, Nasarawa 13, Taraba 10, Benue 9 sai kuma Ebonyi mai 8.

Sauran sun hada da Zamfara mai mutane 7, Plateau 5, Edo da Akwa Ibom da Lagos na da bibiyu, sai kuma Jihohin Oyo da Imo da Rivers da Cross Rivers da Ogun da Bayelsa da Delta da kuma Kebbi dake da guda-guda.

Continue Reading

Talla

Trending

%d bloggers like this: