Wani mutum da ke fama da cutar Ebola a jamhuriyar ta Congo ya tsere daga cibiyar lafiya inda yake karbar kulawa.
Mutumin da ba’bayyana sunanshi ba kamar Yadda Mujallar Alumma ta rawaito tace Ma’aikatar lafiya ta kasar ta tabbatar da faruwar lamarin inda ta bayyana hukumomi a kasar ta Congo. sun ce suna kyautata zaton mara lafiyar ya koma cikin jama’a.
Wanda lamarin zai iya haifar da gagarumar koma baya ga yunkurin kawo karshen cutar a kasar.
Hukumar lafiya ta duniya (WHO) dai tuni ta tabbatar da barkewar cutar Ebola a baya bayanan a kasar ta Congo a matsayin matsalar kiwon lafiya da ya shafi duniya baki daya.
Wannan dai shi ne barkewar cutar Ebola na biyu da ya fi kamari a kasar, inda izuwa yanzu an samu mutane kimanin 2500 da suka kamu da cutar a kasar ta Congo

Leave a Reply

%d bloggers like this: