Dan wasan kungiyar Liverpool kuma dan kasar Senegal, Sadio Mane, ya zama gwarzon dan kwallon nahiyar Afrika na shekarar 2019 a taron bikin da aka shirya ranar Talata, 7 ga watan Junairu, a kasar Masar.

Dan shekara 27 yayi takara da abokin wasansa a Liverpool, Mohamed Salah da dan kwallon Manchester City, Riyad Mahrez.

Ga jerin gwarazan:

Gwarzon dan kwallon Afrikan shekara Sadio Mane (Senegal da Liverpool)

Gwarzuwar ‘yar kwallon Afrikan shekara Asisat Oshoala (Nigeria & Barcelona)

Matashin dan kwallon shekara Achraf Hakimi (Morocco & Borussia Dortmund)

Kocin Afrikan shekara (Maza) Djamel Belmadi (Algeria)

Kocin Afrikan shekara (Mata) Desiree Ellis (South Africa)

Gwarzuwar kasa, shekarar 2019 Algeria Dan kwallon da yaci kwallo mafi kyau a shekara Riyad Mahrez

‘Yan kwallo 11 mafi kyau a Afrika

Andrey Onana,

Achraf Hakimi,

Kalidou Koulibaly,

Joel Matip,

Serge Aurier,

Riyad Mahrez,

Idrissa Gueye,

Hakim Ziyech,

Mohamed Salah,

Sadio Mane,

Pierre Emerick-Aubameyang

Muryar Yanci/matashiya

Leave a Reply

%d bloggers like this: